Shugaban hukumar kwallon kafa ta ƙasa NFF, Amaju Pinnick, ya dakatar da aniyarsa ta neman wa’adi na uku a matsayin shugaban hukumar kwallon kafa ta Najeriya.
Idan za a iya tunawa dai tun bayan da Super Eagles ta kasa samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya da za a yi a kasar Qatar a watan Nuwamba, ‘yan Najeriya da dama ke yin shaguɓe akan shugaban NFF ya yi murabus daga mukaminsa tare da mambobin hukumarsa.
Sai dai kuma mai kula da kwallon kafa na Warri, haifaffen jihar Delta, yayin da ya dage kan ganin cewa, zai sake tsayawa takara a karo na biyu, wanda zai shafe watanni masu zuwa, ya ce, ba zai sake neman tazarce ba sabanin matsayinsa na tsayawa takara karo na uku.
Da yake magana a gidan talabijin na Arise, shugaban hukumar ta NFF, ya bayyana matsin lamba daga iyalansa a matsayin dalilin da ya sa ya ki amincewa da ajandar wa’adi na uku.