Majalisar kasar Pakistan ta zabi Shehbaz Sharif a matsayin sabon firaministan kasar, bayan da ta kada kuri’ar rashin amincewa da mulkin Imran Khan da safiyar Lahadi.
A yanzu Shehbaz Sharif zai kafa sabuwar gwamnati wadda za ta mulki kasar zuwa watan Agustan 2023, lokacin da ake sa ran gudanar da zabuka a kasar.
Mista Sharif zai kasance firaministan Pakistan na 23 cikin jerin firaministocin da suka mulki kasar.
Abokin hamayyarsa Shah Mahmood Qureshi ya sanar da cewa, jam’iyyarsa ta Pakistan Tehreek-e-Insaf, za ta kauracewa zaman majalisar, kuma mambobinta sun fice daga zauren majalisar.