fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Rundunar ƴan tsanda ta haramtawa jami’an ta sanya kayan gida

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da haramta sanya tufafin da ba a amince da shi ba ga jami’an ta, domin gudanar da ayyuka na yau da kullum.

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP Usman Alkali Baba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta wallafa a yammacin ranar Juma’a.

Ya kuma umarci rundunar ‘yan sanda X-Squad da jami’an sa ido, domin tabbatar da aiwatar da umarnin.

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP Usman Alkali Baba, ya bayyana takaicin sa kan yadda jami’an ‘yan sandan da ke sintiri da masu gadi da tsayawa da bincike da sauran ayyukan ‘yan sanda suka saba wa ka’idar sanya rigar da aka amince da ita a Najeriya.

Ya kara da cewa, a yayin sintiri, jami’an ‘yan sanda sun samu dabi’ar sanya rigar gida da huluna musamman ma, “Jami’ai na musamman, Commando da MOPOL da kuma SCORPION da sauran su yayin da suke bakin aiki”.

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa, ta bayar da umarnin cewa, dukkan sassan ’yan sanda musamman na Force Provost Marshal, IGP X-Squad da Monitoring Unit da su tabbatar da aiwatar da tsauraran umarnin tare da sanya takunkumi mai tsanani ga jami’an da suka yi karya doka.

“Dukkan jami’an sa ido za su fuskanci hukunci mai tsanani idan har jami’an da ke karkashinsu suka karya wannan umarni,” in ji shi.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...

Kwallaye 6 da aka zurawa Santos a raga ta sanya Neymar ya fashe da kuka

Ɗan wasan tawagar Brazil, Neymar ya fice daga cikin...

Hukumar Shari’a ta magantu kan sadakin dubu 20 da ya yamutsa hazo a Kano

Hukumar shari’a ta jihar Kano, ta ce ba a...

Cutar Mashako ta yi ajalin Yara hudu a Kano

Rahotanni na cewa cutar mashaƙo wadda aka fi sani...

Cin zaben da NNPP ta yi a Kano cuwa-cuwa ne – Ata

Ministan Jiha na Gidaje da Cigaban Birane, Rt Hon...

Mutane kusan 40 sun ɓace sakamakon haɗarin kwale-kwale a Sokoto

Aƙalla mutum 40 ne ake nema bayan haɗarin kwale-kwale...

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi...

Ba mu yarda da zaben Ghari da Tsanyawa ba – NNPP

Jam'iyar NNPP mai mulkin jihar Kano a arewacin Najeriya...

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...
X whatsapp