fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Rundunar ƴan tsanda ta haramtawa jami’an ta sanya kayan gida

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da haramta sanya tufafin da ba a amince da shi ba ga jami’an ta, domin gudanar da ayyuka na yau da kullum.

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP Usman Alkali Baba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta wallafa a yammacin ranar Juma’a.

Ya kuma umarci rundunar ‘yan sanda X-Squad da jami’an sa ido, domin tabbatar da aiwatar da umarnin.

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP Usman Alkali Baba, ya bayyana takaicin sa kan yadda jami’an ‘yan sandan da ke sintiri da masu gadi da tsayawa da bincike da sauran ayyukan ‘yan sanda suka saba wa ka’idar sanya rigar da aka amince da ita a Najeriya.

Ya kara da cewa, a yayin sintiri, jami’an ‘yan sanda sun samu dabi’ar sanya rigar gida da huluna musamman ma, “Jami’ai na musamman, Commando da MOPOL da kuma SCORPION da sauran su yayin da suke bakin aiki”.

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa, ta bayar da umarnin cewa, dukkan sassan ’yan sanda musamman na Force Provost Marshal, IGP X-Squad da Monitoring Unit da su tabbatar da aiwatar da tsauraran umarnin tare da sanya takunkumi mai tsanani ga jami’an da suka yi karya doka.

“Dukkan jami’an sa ido za su fuskanci hukunci mai tsanani idan har jami’an da ke karkashinsu suka karya wannan umarni,” in ji shi.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp