fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: PDP ta dakatar da shugabanta a Zamfara

Date:

Jam’iyyar PDP reshen jihar Zamfara ta sanar da dakatar da Kanar Bala Mande mai ritaya har sai an kammala bincike kan zargin da ake masa.

A cewar sanarwar da sakataren yada labaran jam’iyyar na jihar, Abba Bello ya fitar ranar Laraba a Gusau, an dakatar da shugaban ne saboda wasu ayyukan da suka saba wa jam’iyyar.

“Hakan ya zama dole saboda shugaban jam’iyyar na gudanar da harkokin jam’iyyar ba tare da sa hannun kwamitin gudanarwa na jihar ba.”

Sanarwar ta kara da cewa, matakin nasa ya sabawa sassa daban-daban na kundin tsarin mulkin PDP.

“Ya zama dole a dakile cin zarafi da kuma karya dokokin tafiyar da jam’iyyar.

“Dakatar da aka yi na tsawon wata daya ne, wannan yana da kyau a baiwa kwamitin aiki damar kafa kwamitin bincike kan zargin”.

“Bisa abubuwan da suka gabata, mataimakin shugaban shiyyar Kaura Namoda, Malam Ali Namoda zai kula da ayyukan jam’iyyar na tsawon lokacin da aka dakatar da shi”.

Bello ya ci gaba da cewa, kwamitin aiki na jihar ya kaddamar da kwamitin bincike domin gudanar da bincike kan wannan zargi.

Mambobin kwamitin sun hada da Ahmed Sani Kaura a matsayin shugaba, Bala Zurmi Member, Sanin Baba memba, Abdulhadi Ahmed memba, Suwaiba Bako Memba Abul Mustapha, da Barr. Ibrahim Jibril zai zama Sakatare.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp