fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: PDP na gudanar da zanga-zanga a Abuja akan sakamakon

Date:

Babbar jam’iyyar hamayya ta PDP na gudanar da wata zanga-zanga a shalkwatar hukumar zaɓen ƙasar INEC a Abuja babban birnin ƙasar.

Shugaban jam’iyyar na ƙasar Iyorchia Ayu, da ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen da aka gudanar gwamna Ifeanyi Okowa na jihar Delta na daga cikin mutanen da suke jagorantar zanga-zangar.

A wata sanarwar da Ibrahim Bashir ɗaya daga cikin shugabannin jam’iyyar ya fitar a madadin daraktan yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar, ya ce daga cikin mutanen da aka gayyata zuwa zanga-zangar sun haɗar da shugaban kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar wato gwamnan jihar Akwa Ibom Udom Emmanuel, da daraktan kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar wanda shi ne gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal.

“Gwamnonin jihohin Bayelsa da Edo da Adamawa da Bauchi da Taraba da kuma Osun States, sauran su ne tsoffin shugabannin majalisar dattawan ƙasar Sanata David Mark da Sanata Abubakar Bukola Saraki, da kwamitin amintattun jam’iyyar da ‘yan majalisar dattawa da na wakilai na jam’iyyar da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar na daga cikin mutanen da suka halarci zanga-zangar”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sanarwar ta kuma umarci jami’an da su sanya baƙin tufafi domin nuna ɓacin ransu a zanga-zangar da za su gudanar a Maitama da ke Abuja.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp