Mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, ya yanki tikitin tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar.
Wani jigo a kungiyar yakin neman zaben sa, Sanata Kabiru Gaya ne ya karbi fom din a madadin sa, mai lamba biyu a ranar Alhamis, 5 ga watan Mayu, in ji rahoton Naija News.
Ku tuna cewa, Osibanjo, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a watan jiya.
Osinbajo dai ya zagaya kasar ne domin tuntubar wakilai gabanin zaben fidda gwani da za a yi a karshen watan nan.
Ziyarar ta baya-bayan nan da Osinbajo ya yi ita ce ranar Laraba lokacin da ya ziyarci jihar Adamawa, inda ya gana da wakilai daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC).