Mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo ya sauka a Kaduna, domin ziyartar wadanda harin jirgin kasa ya rutsa da su a ranar Litinin.
‘Yan ta’adda sun kai hari kan jirgin a ranar Litinin din da ta gabata, inda suka kashe mutane da dama tare da yin awon gaba da wasu da dama, an kai harin ne a kusa da yankin Kateri-Rijana na jihar.
‘Yan bindigar sun tarwatsa titin jirgin da wata mota kirar IED bayan sun kai farmaki kan fasinjojin.
Osinbajo ya samu tarba daga gwamnan Kaduna Nasir el-Rufai da Samuel Aruwan kwamishinan tsaro na cikin gida.