Akalla mutane uku ne suka mutu, wasu da dama kuma suka jikkata, a lokacin da wata fashewa ta afku a wani wurin shan ruwa a Kabba, jihar Kogi.
Lamarin wanda ya afku a ranar Laraba a kewayen mahadar Lewu, ya lalata kayayyaki da dukiyoyi.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi har yanzu ba ta ce uffan a hukumance kan wannan lamarin ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya rawaito cewa, jaridar PlatinumPost ta bayar da rahoton cewa, a baya-bayan nan kungiyar IS da ke yammacin Afirka (ISWAP) ta dauki alhakin harin da aka kai ofishin ‘yan sanda a yankin Okene na jihar Kogi, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane hudu ciki har da jami’ai.
A kasa akwai wasu hotuna daga lamarin.

