fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ministoci 10 na Buhari sun yi murabus

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya yi ban-kwana da ministocinsa da suka ajiye aiki don yin takara a babban zaɓe mai zuwa na 2023.

Yayin jawabinsa a ranar Juma’a, Buhari ya ce ya yi imani da yawa daga cikin ministocin na da ƙwarewar da za su iya gadarsa.

“Babu wata tantama idan aka samu shugaban ƙasa daga cikin ministocin nan za a ga cikakkiyar ƙwarewa da kuma tsabar aiki ga al’umma,” in ji shi.

“Wannan na ɗaya daga cikin tarihin da za mu bar wa ‘yan Najeriya.”

A ranar Laraba ne Shugaba Buhari ya umarci dukkan ministoci da shugabannin hukumomi da ma’aikatu masu son tsayawa takara a muƙamai daban-daban da su ajiye ayyukansu nan da ranar Litinin mai zuwa.

Daga cikin ministocin da suka yi ban-kwana da shugaban a ranar Juma’a har da Ministan Shari’a Abubakar Malami, wanda rahotanni ke cewa zai yi takarar gwamna a jiharsa ta Kebbi.

Ministocin su ne:

  • Ministan Shari’a Abubakar Malami
  • Ministan Sufuri Rotimi Amaechi
  • Ministan Ƙwadago Chris Ngige
  • Ƙaramin Ministan Man Fetur Timpre Sylva
  • Ministan Neja Delta Godswill Akpabio
  • Ministan Kimiyya da Fasaha Ogbonnaya Onu
  • Ministar Harkokin Mata Pauline Tallen
  • Ƙaramin Ministan Ma’adanai, Uche Ogah
  • Ministan Kimiyya da Fasaha Ogbonnaya Onu
  • Ƙaramin Ministan Neja Delta Tayo Alasoadura.

Shugaba Buhari wanda ya ɗare mulki a 2015 zai kammala wa’adin mulkinsa nea watan Mayun 2023, yayin da za a yi zaɓukan ƙasar kuma a Fabrairun 2023.

Ana sa rana jam’iyyun siyasa za su gudanar da zaɓukan fitar da gwani kafin ranar 3 ga watan Yunin 2022. In ji BBC.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...
X whatsapp