Majalisar dokokin jihar Ebonyi, a ranar Litinin, ta bayyana kujerar mataimakin kakaki, Odefa Obasi Odefa, a matsayin ba kowa bisa zargin ya yi murabus.
Vanguard ta rawaito, cewa, mambobin biyu a majalisar, Oliver Osi, mai wakiltar mazaɓar Ivo da kuma Ngozi Ezilo, mai wakiltar Afikpo North East, sun sauya sheka daga PDP zuwa APC.
A zaman majalisar na ranar Litinin da ta yi, lamarin ya tayar da hatsaniya, yayin da mutane uku baki ɗaya suka musanta ikirarin majalisa, suna nan daram a matsayin su.
Rikicin siyasa na cigaba da ƙamari a majalisar dokokin jihar, tun bayan sauya shekar gwamnan Dave Umahi.A cewar kakakin majalisar bayan karanta wasikar mutanen biyu, sun kuma yi murabus daga kasancewarsu mambobin majalisar dokokin jihar Ebonyi.
Sai dai lamarin ya tada hatsaniya, yayin da mutanen uku baki ɗaya suka musanta ikirarin majalisa, suna nan daram a matsayin su.