fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Masu garkuwa sun yi awon gaba da mutane da dama a Abuja

Date:

An yi garkuwa da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba a Abuja, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a cikin gidajensu da sanyin safiyar ranar Litinin.

Gidan da aka kai harin yana unguwar Gwarinpa ne a Abuja, babban birnin tarayya, inji rahoton Naija News Hausa.

‘Yan bindigar wadanda aka ce sun zo ne da wasu makamai da suka hada da baka, kibau, da adduna, sun gudanar da aikin ne a yankin tsakanin karfe daya na safe zuwa karfe hudu na safe.

Da yake bayyana hakan, wani mazaunin garin mai suna Mohammed ya shaida wa Aminiya ta wayar tarho cewa, ‘yan bindigar sun samu shiga Estate ne, bayan Efab Queens da ke 6th Avenue, Gwarinpa.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Josephine Adeh, ta bayyana faruwar lamarin a matsayin na fashi da makami ba wai na garkuwa da mutane ba.

Ta kara da cewa, an tattara jami’an ‘yan sanda zuwa wurin da lamarin ya faru tare da yin alkawarin bayyana sakamakon binciken su ga jama’a da zarar an samu karin haske.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp