Ƙasar Masar ta samu nasarar kaiwa ga wasan ƙarshe na gasar cin kofin Nahiyar Afrika, bayan da ta doke mai masaukin baki a bugun daga kai sai mai tsaron raga.
Mai tsaron ragar Masar Gabaski ne ya doke bugun daga kai sai mai tsaron raga guda biyu yayin da ɗan wasan Kamaru ya buga ƙwallo ta uku a waje, lamarin da ya sanya Masar ta samu nasara da ci 3-1 a wasan.
A ranar Lahadi ne Masar za ta kara Senegal a wasan ƙarshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika.