Malaman Makarantun Firamare da Sakandare na gwamnati a jihar Akwa Ibom sun fara yajin aikin sai baba-ta-gani, don neman biyan bukatunsu na biyan kudin hutun shekara takwas da basukan karin shekaru shida.
Sakataren kungiyar malamai ta ƙasa ta jihar, Victor Amirize, ya bayyana hakan a wata sanarwa, cewa yajin aikin ya fara aiki ne daga tsakar daren ranar Talata, ya kuma kara da cewa kungiyar ta cimma matsayar ne bayan “dukkan hanyoyin tattaunawa da shawarwarin sulhu sun gaza daga bangaren gwamnatin jihar.”
Amizire ya zayyana bukatun malaman jihar da suka hada da, “biyan 2013, 2015, 2016, 2017, 2018, 2019, 2020 da kuma 2021 na barin tallafi ga malaman firamare.”
“Kungiyar Malamai ta Najeriya (NUT) a nan ta umurci dukkan malaman makarantun firamare da sakandare a makarantun gwamnati da su ci gaba da yajin aikin da ba a taba gani ba,” in ji shugaban kungiyar.