Majalisar dokokin jihar Kano, ta umurci kwamitinta na kula da harkokin wasanni da ya binciki ficewar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars daga gasar kwallon kafa ta Najeriya NPFL.
Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin mahimmancin jama’a da Alhaji Nurudeen Alhassan (APC-Rano) ya gabatar yayin zaman majalisar na ranar Litinin a Kano.
Da yake gabatar da kudirin, Alhassan, kuma shugaban kwamitin riko na majalisar, ya bayyana wasanni a matsayin ginshikin ci gaban matasa.
A cewarsa, ficewar Kano Pillars daga NPFL wani lamari ne mai ban tausayi wanda dole ne a yi bincike sosai don hana afkuwar lamarin nan gaba.
Majalisar ta amince da kudirin baki daya, sannan ta bukaci kwamitin da ke kula da harkokin wasanni da ya gudanar da bincike tare da bayar da rahoto cikin makonni biyu domin ci gaba da aiwatar da dokar.