Sanata Ahmad Babba Kaita na jam’iyyar APC, Katsina ta Arewa, mai wakiltan shugaba Buhari a majalisar dattawa ya fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP.
Wannan mataki dai na iya nuna cewa, an samu sauyi a siyasar jihar, wanda ke hannun PDP har zuwa 2015.
Kaita ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC mai mulki a wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Malam Abdulkadir Lawal ya fitar.
Majalisar dattawan ta ƙunshi kananan hukumomi 12, ciki har da Daura, mahaifar Buhari.
An zabi Babba Kaita a majalisar dattawa ta 8 a shekarar 2018 domin cike gurbi a shiyyar sanata bayan rasuwar Sanata Mustapha Bukar.
An sake zaben shi ne a 2019.