Daya daga cikin alhazai 668 da suka fito daga jihar Taraba zuwa aikin hajjin da aka kammala a kasar Saudiyya, an sanar da batan ta.
An bayyana cewa, mahajjaciyar da ta bace mai suna Hassana Abdullahi Bamuze ya bace daga cikin rukunin alhazai biyu da suka isa jihar.
Da yake tabbatar da rahoton ranar Asabar a Jalingo, babban birnin jihar, jami’in hulda da jama’a na hukumar jin dadin alhazai ta jihar, Baba Hamza Muri, ya ce, har yanzu ba a gano mahajjaciyar mace da ta bace ba.
Hukumar ta ce, an samar da hanyoyin da suka dace don gano ta kuma ta yarda cewa “Hukumar Hajji ta Najeriya ta ba da tabbacin cewa za su yi duk mai yiwuwa don taimaka mana mu gano ta.”
Ya ce, jihar ta kammala aikin Hajjin shekarar 2022 cikin nasara tare da isar da kaso na karshe na maniyyata 131 daga kasar Saudiyya a yau.
“Alhazan jihar sun fara komawa gida ne bayan kammala aikin Hajji tare da alhazai 536 a ranar Asabar da ta gabata, hukumar ta yi farin ciki da cewa aikin ya samu nasara.”