A ranar Laraba ne Kotun Koli ta tabbatar da zaman gidan yari na tsawon shekaru shida bayan daure tsohon Daraktan Fansho na Tarayya (FDP), Mista John Yakubu Yusuf, sannan ta kuma umarce shi da ya mayar wa gwamnatin tarayya Naira biliyan 22.9.
Makudan kudin Naira 22.9 na daga cikin asusun fansho na ‘yan sanda da aka shigar da kara a gaban wata babbar kotun tarayya da ke babban birnin tarayya Abuja cewa an karkatar da su.
Mai shari’a Tijjani Abubakar a hukuncin da kotun daukaka kara a kan Yusuf, ya tabbatar da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke wa a shekarar 2018 ta yanke masa hukuncin daurin shekaru shida a gidan yari, baya ga maido da makudan kudade.
Kotun kolin ta ce, Yusuf da wasu da ke aikata zamba dole ne a fada masu ta hanyar yanke hukunci a kotu cewa, yanzu ba aiki ba ne kamar yadda aka saba.