fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Kotu ta kori karar sauke gwamna da mataimakin sa

Date:

Kotun daukaka kara reshen Enugu, a ranar Juma’a ta kori karar da ke neman a kori Gwamna David Umahi da mataimakinsa Kelechi Igwe daga ofis, saboda sauya sheka zuwa wata jam’iyya.

A watan Nuwamba 2020 Messrs Umahi da Igwe sun sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressive Congress (APC) daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

Bayan sauya shekar tasu, dan takarar jam’iyyar APC a zaben gwamna na 2019, Sonni Ogbuoji, da mataimakinsa, Justin Mbam, sun garzaya wata babbar kotun jihar Ebonyi suna neman ta kori gwamnan da mataimakinsa.

Masu shigar da kara sun bukaci kotun da ta bayyana kujerar gwamna a matsayin wanda ba kowa, saboda sauya shekar mutanen biyu daga PDP zuwa APC.

Messrs Ogbuoji da Mbam sun kuma bukaci kotun da ta bayar da umarnin a rantsar da su cikin gaggawa tunda sun zo na biyu a zaben gwamna na 2019.

Amma babbar kotun da ta yanke hukunci a ranar 28 ga watan Fabrairu ta kori karar tare da bayar da Naira 500,000 a matsayin diyya ga wanda ya shigar da karar.

Ba su gamsu da hukuncin ba, masu gabatar da kara sun daukaka kara kan hukuncin.

A hukuncin da ta yanke, a ranar Juma’a, kotun daukaka kara ta amince da hukuncin da karamar kotun ta yanke kan lamarin.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp