Kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar Nasarawa, a ranar Litinin, ta soke nasarar Gwamna Abdullahi Sule.
Kwamitin mutum uku karkashin jagorancin mai shari’a Ezekiel Ajayi, yayin da yake yanke hukuncin ta hanyar zurfafa bincike, ya ce Emmanuel Ombudagu na jam’iyyar PDP ne ya lashe zaben.
Biyu daga cikin alkalan sun amince cewa PDP ce ta lashe zaben yayin da alkali daya ya ki amincewa.
Ezekiyel ya ci gaba da cewa wanda ya shigar da karar ya iya tabbatar da hujjarsa babu shakka.
Tsohon gwamna Abdullahi Adamu da Tanko Al-makura na daga cikin jiga-jiganƴan siyasa da suka halarci kotun.
Ku tuna cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Lafiya, ta bayyana Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar Nasarawa a watan Maris.
Farfesa Ishaya Tanko, jami’in zabe na INEC ya bayyana cewa dan takarar APC ya samu kuri’u 347,209 inda ya doke abokin hamayyarsa David Ombugadu, dan takarar jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 283, 016.