fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’in Birtaniya sun tsare Peter Obi

Date:

Kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, ya ce, jami’ai sun tsare tare da hantarar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar, Peter Obi a birnin London.

Mai magana da yawun kwamitin kamfe na jam’iyyar LP, Diran Onifade ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Laraba.

Sanarwar ta ce, lamarin ya faru ne a filin jirgin sama na Heathrow da ke London.

Ta ƙara da cewa jami’an shige da fice na Birtaniya ɗin ne suka titsiye tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa.

Karanta Wannan: Ɗan takarar mu Obi ake hari ba jam’iyyar mu ba – LP

Diran Onafide ya ce, hukumomi a Birtaniya sun tsare tare da yin tambayoyi ga tsohon gwamnan na jihar Anambra kan wani lamari da ya shafi wani mutum da ke yin sojan-gona da suna Peter Obi.

Sanarwar ta ƙara da cewa, jami’an sun sassauta wa Petetr Obi ne bayan wasu ƴan Najeriya da ke a filin jirgin sun sanya baki.

Peter Obi dai ya isa birnin na London ne, domin bukukuwan Easter na mabiya addinin Kirista.

Bayanin ya nuna cewa, bayan saukar Peter Obi a filin jirgin na Heathrow da ke London, jami’an tsaro sun zo wurin sa a lokacin da yake kan layin tantancewa, tare da miƙa masa wata takarda da ke ƙunshe da umurnin tsarewa, sannan suka buƙace shi da ya fita daga layi.

Onifande ya ce, jami’an sun yi wa Peter Obi tambayoyi na tsawon lokaci, wanda abu ne da ba a saba ganin ya faru ga wani mutum da ya kwashe sama da shekara 10 yana rayuwa a ƙasar ba.

Sai dai mutane ƴan asalin Najeriya sun rinƙa ɗaga muryoyinsu, domin sanin dalilin da ya sa aka tsare tsohon gwamnan.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp