fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: INEC ta tabbatar da Machina maimakon Lawan

Date:

Hukumar zabe mai zaman kanta ta tabbatar da Bashir Machina a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress mai wakiltar mazabar Yobe ta Arewa.

Wani tabbataccen kwafin rahoton INEC na ranar 28 ga Mayu, 2022, zaben ya nuna Machina ya samu kuri’u 289 cikin wakilai 300, wanda hakan ke tabbatar da ikirarin da ‘yan siyasar ke yi na cewa, shi ne ya lashe zaben fidda gwani kuma ya yi takara a bisa doka.

Takardar wacce ofishin zabe ta tabbatar a ranar 23 ga watan Yuni, 2022, ba ta ambaci Ahmad Lawan ba, shugaban majalisar dattawan da ya yi ta kokarin karɓe wa Machina aiki tare da shugaban jam’iyyar na kasa Abdullahi Adamu.

Adamu ya sanya sunan Lawan a matsayin dan takarar jam’iyyar APC a zaben Sanatan Yobe ta Arewa da aka shirya gudanarwa a watan Fabrairun 2023, yana mai cewa an gudanar da zaben fidda gwani a asirce inda ake zargin Lawan ya yi nasara.

Ko da yake Machina ya samu shaidar lashe zaben, amma har yanzu yana sa ran za a kara gwabzawa lokacin da INEC za ta tsayar da ‘yan takarar da za su tsaya takara a jam’iyyun siyasa daban-daban a makonni masu zuwa. INEC ta ce ba ta da hurumin zabar dan takara a zabe, duk da cewa tantance ta ya zama dole don tabbatar da an gudanar da zabe.

Lawan ya fara yunkurin kwace tikitin ne daga hannun Machina, bayan ya sha kaye a babban taron jam’iyyar da ke mulki, wanda Bola Tinubu ya samu nasara a ranar 8 ga watan Yuni.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp