fidelitybank

Da Ɗumi Ɗumi: Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24

Date:

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a kananan hukumomin Jema’a da Kaura tare da fara aiki nan take biyo bayan shawarwarin da jami’an tsaro suka bayar, bayan wani hari da wasu da ake kyautata zaton Fulani ne suka kai wa yankin Agban Kagoro da kewaye wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi.

Sanarwar da Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya fitar ta bayyana cewa, “Bayan shawarwarin da hukumomin tsaro suka bayar, gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a kananan hukumomin Jema’a da Kaura tare da fara aiki nan take. Hakan na nufin taimaka wa jami’an tsaro wajen daidaita al’amura a yankunan, da ceton rayuka da dukiyoyi da kuma ba da damar maido da doka da oda.”
Sanarwar ta kuma bayyana cewa hukumomin tsaro na da cikakken ikon aiwatar da dokar hana fita.

Gwamnati ta yi kira ga daukacin mazauna kananan hukumomin Jema’a da Kaura da su ba jami’an tsaro hadin kai a aikin gaggawa na maido da zaman lafiya da bin doka da oda.

Sai dai gwamnatin, a cewar sanarwar, ta yi Allah-wadai da tashe-tashen hankula da duk wasu ayyukan rashin bin doka da ya afku a yankin.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp