Gwamnatin tarayya ta bayyana fatan ganin kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta janye yajin aikin gargadi da ta ke yi na tsawon makonni hudu a wannan mako.
Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Sanata Chris Ngige ne ya bayyana hakan a lokacin da ya ke jawabi ga manema labarai, bayan kammala taron sasantawa tsakanin gwamnati da kungiyar ASUU na karshe.
Ngige ya ce, taron ya amince da abubuwa da dama tare da sanya lokacin aiwatar da yarjejeniyar. A cewarsa, ASUU ta amince su koma ga mambobinsu da tayin gwamnati tare da kawo masa rahoto kafin ya kare a makon nan.
Ministan ya sake nanata cewa da yawa daga cikin abubuwan da ke cikin yarjejeniyar aiki ta 2020 (MOA) an yi su sosai a yayin da ake magance wasu.
Ya ce, “Muna da fanni daya ko biyu da suka saba. Ɗaya daga cikin sababbin wuraren shine sake yin shawarwari game da sharuɗɗan ayyuka, wanda ake kira yarjejeniyar 2009. An cimma yarjejeniya a shekara ta 2009 cewa za a sake duba yanayin hidimar su duk bayan shekaru biyar. An yi shi a cikin 2014.