Sakataren kwamitin riko da tsare-tsare na musamman na jam’iyyar APC, Sanata John Akpanudoedehe, ya tabbatar da cewa, a ranar Litinin mai zuwa ne jam’iyyar za ta fara sayar da fom ga duk masu neman tsayawa takarar mukaman kasa gabanin zaben da za a yi a ranar 26 ga watan Fabrairu za a gudanar da babban taron jam’iyyar na kasa.
Jadawalin ayyukan kamar yadda Akpanudoedehe ya fitar a ranar Lahadi, ya ce, za a yi siyan fom ne kawai a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja.
“An fara sayar da fom ga duk masu neman mukamai na kasa a ranar Litinin 14/02/2022, a sakatariyar jam’iyyar APC ta kasa. A cewar sa.
Tuni dai wasu daga cikin jiga-jigai na ƴaƴan jam’iyyar ta APC su ka nuna sha’awar su ta tsaya takarar shugabanci.