Jam’iyyar APC mai mulki ta tura kujerar shugabancin jam’iyya ga yankin Arewa gabanin zaben 2023 mai zuwa.
Gwamna Nasiru El-Rufai na jihar Kaduna da Atiku Bagudu na jihar Kebbi ne, suka bayyana hakan a lokacin da suke amsa tambayar jaridar Daily Trust, a wani taron manema labarai da suka gudanar bayan ganawa da shugaba Buhari game da lamurran jam’iyyar.
El-Rufai ya ce, jam’iyyar ta amince da sauya mukaman da ba kowa akansu a kwamitin ayyuka na kasa (NWC) ga tsakanin sassan Arewa da Kudancin kasar nan gabanin taron gangamin jam’iyyar APC na kasa na ranar 26 ga Maris.
Kenan za a iya cewa, mukamin shugabancin jam’iyyar wanda tsohon Gwamna John Odigie-Oyegun da Adams Oshiomhole na Jihar Edo daga yankin Kudu suka rike zai koma yankin Arewa.