Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki ta dage zaben fidda gwani na shugaban kasa da ta shirya gudanarwa a ranar Litinin 23 ga watan Mayu 2022.
Ba a bayar da dalilin dage zaben ba. In ji Blue Print.
Kimanin ‘yan takara 25 ne ke fafatukar neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki.
Wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa, Barista Felix Morka ya fitar a daren Lahadi, ta ce nan ba da jimawa ba za a sanar da sabon ranar da za a gudanar da atisayen.
A takaice dai sanarwar ta ce: “An dage taron tantance ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da aka shirya tun farko a ranar Litinin, 23 ga Mayu, 2022.