Jam’iyyar APC mai mulki ta ɗage babban taronta na ƙasa da ta shirya gudanarwa a wannan watan ban Fabrairu.
Daily Trust ta rawaito cewa, tun farko dai APC ta tsara gudanar da taron a ranar 26 ga watan Fabrairu, 2022, amma lamarin raba kujerun shugabanni zuwa yanki-yanki da kuma rikici a wasu jihohi suka hana jam’iyyar motsa wa.
A wata wasika mai ɗauke da kwanan watan 21 ga watan Fabrairu, 2022, kwamitin rikon kwarya na APC ta kasa ya sanar da hukumar zaɓe INEC ci gaban da a ka samu na ɗage taron.
Wasikar da Jam’iyyar ta aike wa INEC kan ɗage taron na ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin rikon kwarya, Gwamna Mala Buni da Sakatarensa, Sanata John James Akpanudoedehe.