fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: An sake kama mutane 2 da suka kai hari Coci

Date:

Biyo bayan harin da aka kai a cocin St Francis Catholic dake garin Owo na jihar Ondo watannin baya, an samu nasarar cafke wasu ‘yan ta’adda biyu da ake zargin ‘yan kungiyar IS ne a yankin yammacin Afirka (ISWAP).

Idan ba a manta ba a ranar Talata ne gwamnan jihar Ondo Oluwarotimi Akeredolu ya tabbatar da cewa an kama wasu ‘yan ta’adda kusan biyar da ke da alaka da harin a jihar.

Kwanaki biyu kacal bayan rahoton, babban rundunar sojin a ranar Alhamis ta bayyana cewa, an kama wasu karin ‘yan ta’adda biyu da suka kashe sama da masu ibada 40 a cocin a ranar 5 ga watan Yuni.

Sanarwar ta fito ne a wata sanarwa da Daraktan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Jimmy Akpor ya fitar.

Da yake bayyana bayanan wadanda ake zargin, Janar Akpor ya ce su ne: Al-Qasim Idris da Abdulhaleem Idris.

Ya bayyana cewa, an kama wadanda ake zargin ‘yan ta’adda ne a Omialafara (Omulafa), karamar hukumar Ose, jihar Ondo, a ranar Talata ta hanyar hadin gwiwa da sojoji da hukumar tsaro ta farin kaya DSS suka yi.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp