Sa’o’i kadan kafin gudanar da taron, dan takarar shugabancin jam’iyyar APC na kasa, Sanata Mohammed Sani Musa, ya bayyana janyewarsa daga takarar, kamar yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba da shawarar.
Mai magana da yawun Musa, Nasir Mohammed, ya tabbatar da hakan a ‘yan mintoci da suka wuce.
Musa, wanda a yanzu haka yake wakiltar Neja ta Gabas a Majalisar Dattawan Najeriya, ya bayyana janyewa daga takarar ne bayan ganawar da masu son tsayawa takara da Shugaba Buhari a ranar Juma’a da sa’o’i 24 zuwa babban taron da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 26 ga Maris, 2022 a Abuja.
Ya yi alkawarin marawa, Sanata Abdullahi Adamu baya a matsayin dan takarar da aka amince da shi.