fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ɗan majalisar Wakilai ya jikkata a taron PDP

Date:

Mutane da dama ne suka jikkata, sakamakon rikicin da ya barke a karamar hukumar Aninri da Nssuka na jihar Enugu yayin taron jam’iyyar PDP.

An tattaro cewa ‘yan barandan da suka jefa kujeru da kwalabe a Nsukka a ranar Asabar din da ta gabata sun yi amfani da makamai cikin ‘yanci a daidai lokacin da mata da wasu suka tsallake rijiya da baya a kokarin tserewa.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa manema labarai cewa, batun wanda ke wakiltar al’ummar Nsukka/Igbo-Eze ta Kudu a Majalisar Wakilai, an ce shi ne ya haddasa rikicin a yayin taron.

Haka kuma a wani taron siyasa da aka gudanar a Ndeaboh a karamar hukumar Aniiri, da dama sun samu munanan raunuka yayin da wasu ke kwance a asibiti sakamakon wani mummunan hari da aka kai a yayin taron siyasa na PDP.

A martanin da ya mayar, tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Ike Ekweremadu, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan rikicin da ya rikide wa taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Aninri ta jihar Enugu a karshen mako da kuma mummunan harin da aka kai wa magoya bayansa da abokan siyasarsa a yayin taron da aka ce a Ndeaboh.

Ekweremadu ya tuna cewa, harin ya bar mutane da dama ciki har da dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Aninri a majalisar dokokin jihar Enugu, Hon. Chinedu Okwu wanda ya samu munanan raunuka, kuma yana kwance a asibiti ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar an gurfanar da wadanda suka aikata laifin.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp