Masu neman tsayawa takara a zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da aka kammala a Filato sun yi zanga-zangar nuna adawa da fitowar Nentawe Yilwatda a matsayin dan takarar jam’iyyar.
‘Yan takarar sun bayyana rashin jin dadinsu da rashin amincewa da zaben fidda gwani a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Danyaro Sarpiya, sakataren ‘Forum of Plateau APC Aspirants’.
Mun rubuta takarda kira ga kwamitin daukaka kara domin a gyara wannan zamba domin ceto jam’iyyar APC a Filato.
“A lokacin zaben fidda gwani, wadanda ba su da izini sun kasance a wurin don tsoratarwa da kuma bin diddigin kuri’un wakilai,” in ji su.