Rahotanni daga jihar Kebbi na cewa ‘yan bindiga sun kashe jami’an tsaro a kalla 19 a wani hari da suka kai a ƙauyen Kanya da ke cikin karamar hukumar Danko-Wassagu.
Maharan sun je ne a kan babura a lokacin da mataimakin gwamnan Kebbi ke ziyara a ƙauyen a ranar Talata.
Mataimakin gwamnan, Sama’ila Yombe Dabai, ya shaida wa BBC cewa, dakarun tsaron sun fafata ne da maharan, amma bai faɗi yawan jami’an da aka kashe ba.
Mutanen da suka mutu sun haɗa da sojoji 13 da ƴan sanda biyar da wani ɗan sa kai.
Maharan sun kuma sace kayan abinci da dabbobi.
Harin ya faru ne kwana ɗaya bayan da ƴan bindiga suka kashe ƴan sa kai 63 a yankin.