fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan ta’adda sun jefa bam ofishin ƴan sandan Kogi

Date:

Wasu ‘yan bindiga da sanyin safiyar Juma’a sun kai harin bam a ofishin ‘yan sanda da ke Eika-Ohizenyi a karamar hukumar Okehi a jihar Kogi, inda suka kashe wani sufeto Jibril da ke bakin aiki.

Wani mazaunin yankin, Malam Momoh Abubakar, ya bayyana cewa, maharan sun mamaye wajen ne da misalin karfe 12:15 na safe dauke da bama-bamai da sauran makamai.

Ya bayyana cewa, bam na farko da suka jefa a cikin ofishin ya yi wani kara mai karfi da ta tada da yawa mazauna wurin, inda ya kara da cewa , bama-baman da suka tayar da wani bangare na ofishin ‘yan sandan.

Abubakar ya kara da cewa, maharan sun samu ranar, domin sun shafe sama da sa’o’i biyu suna gudanar da ayyukansu ba tare da tsangwama daga jami’an tsaro ko jama’ar gari ba.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kogi, Edward Egbuka, ya ce, ya ba da umarnin tura karin kadarorin aiki, wadanda suka hada da jami’an rundunar ‘yan sanda na sashin yaki da ta’addanci, sashin amsa gaggawa, ofishin leken asiri na jihar tare da hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro don dawo da zaman lafiya yankin. In ji Daily Trust.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP William Aya, wani bangare na ofishin rundunar ‘yan sandan yankin ya kone kurmus da maharan suka yi amfani da su.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...
X whatsapp