fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan ta’adda sun harbe matafiya 5 har lahira a Katsina

Date:

An bayar da rahoton mutuwar fasinjoji biyar tare da raunata wasu uku bayan da wasu ‘yan bindiga suka bude wuta kan wata mota a kan hanyar Yan Tumaki zuwa Danmusa a jihar Katsina, da safiyar Asabar.

Karamar hukumar Danmusa dai na daya daga cikin yankunan da ake fama da matsalar tsaro a jihar Katsina, inda ta raba iyaka da dajin Rugu da ake fargabar da kuma yankunan Safana, Kankara da sauran al’ummomi a jihar Zamfara inda ‘yan fashi ke yawan kai farmaki.

Wani ganau wanda ya bayyana sunansa da Musa ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa, yawancin fasinjojin sun fito ne daga Benin a Jihar Edo yayin da daya ke dawowa daga Babban Birnin Tarayya (Abuja) inda ya je kawo kaji.

Ya ce, fasinjojin ‘yan asalin garin Gobirawa ne da Kaigar Malamai a jihar Katsina.

“Motar mai kirar Golf ce, ta taso daga Yantumaki zuwa garin Danmusa da safe. Fasinjojin sun kwana a Yantumaki, saboda sun isa can da daddare. Da safe suka hau motar zuwa garin Danmusa inda zasu dauki babura zuwa garuruwansu.

“Amma an kai wa motar harin ‘yan mintoci kadan da barin Yantumaki. Abin da ya faru shi ne ‘yan fashin sun hango motar inda suka yi kokarin tsayar da motar amma direban ya ki tsayawa, lamarin da ya sa ‘yan bindigan suka fara harbin su. Motar ta yi damina ta bugi bishiya,” inji shi.

Musa ya ce, barayin sun gudu ne a lokacin da hatsarin ya afku.

“An kuma sanar da ‘yan sanda a Danmusa, inda suka dauko gawarwakin, kuma suka kai wadanda suka jikkata uku asibiti. Mun yi jana’izar wadanda suka mutu, yayin da sauran mutane uku ke karbar kulawar lafiya,”

Musa ya kara da cewa. Dalilin harin
Wata majiya da ke zaune a yankin amma ba ta so a bayyana sunanta, ta ce, ‘yan bindigar na kara kai hare-hare mai yiwuwa, domin daukar fansa kan jami’an tsaro da suka far musu.

Hatta kisan da aka yi wa fasinjojin an ce ‘yan fashin sun fusata ne, saboda ‘yan sanda da sojoji sun hana su satar shanu masu tarin yawa a ranar Alhamis din da ta gabata.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp