fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan sanda sun murƙushe ƴan IPOB a wani artabu

Date:

Rahotanni sun tabbatar da cewa, an kashe wasu da ake zargin ƴan kungiyar masu fafutukar kafa ƙasar Biafra IPOB, a wani artabu da ‘yan a garin Omuma, mahaifar gwamna Hope Uzodimma da sanyin safiyar Lahadi.

An kashe ‘yan bindigar ne bayan sun kai hari ofishin ƴan sandan Omuma da ke karamar hukumar Oru ta Gabas a jihar Imo, kamar yadda CSP Mike Abattam, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Imo ya bayyana.

Ya ce, ƴan bindigar sun buɗe wuta bayan sun abka ofishin ƴan sanda da safe, amma a cewarsa ƴan sanda sun murƙushe su a musayar wuta.

Jami’in ya ce, mutum huɗu aka kashe yayin da wasu saura suka tsere cikin daji raunuka a jikinsu.

Wannan na zuwa ne bayan wasu ƴan bindiga sun kai hari ofishin ƴan sanda a Umuguma da ke yankin Owerri ta Yamma tare da kashe ƴan sanda biyu a ranar Asabar.

Haka kuma ƴan bindigar sun kai hari gidan shugaban ƴan ƙabilar Igbo ta Ohanaeze Ndigbo inda suka ƙone gidansa a jiya Asabar.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp