Yayin da matsalar tsaro ta yi ƙamari Najeriya tare da ci gaba ta’azzara, ‘yan majalisar wakilan kasar sun ce, za su tafi yajin aiki har sai sun ga canji a al’amuran da suka jibanci tsaro.
Hon Aminu Sulaiman Goro, daya ne daga cikin ‘yan majalisar ya shaida wa BBC cewa, kullum suka zauna zaman majalisar suna samun rahotannin matsalar tsaro iri-iri.
Ya ce, kuma tabarbarewar tsaron ta fi zafi daga bangaren Arewacin Najeriya, shi ya sa kusan kullum sai sun yi muhawara a kan abin da ya shafi tsaro.
Dan majalisar, ya ce” Irin masifun da ake shiga a ce yau an kashe mutane, gobe an sace mutane jibi an kona mutane, masifar ta kai ga cewa tsaro ya lalace.”