A safiyar yau Asabar ne dai wai ƴan bindiga su ka ƙone gidan Babban Shugaban kungiyar inyamirai ta Ohaneze Ndigbo, Farfesa George Obiozor a Awo-Omanma, Ƙaramar Hukumar Oru ta Kudu a Jihar Imo.
An kiyo cewa maharan da su ka zo gidan Shugaban a ababen hawa, sun jefa bamabamai cikin gidan.
Sai dai kuma rahotanni sun baiyana cewa Obiozor ba ya gidan lokacin da s ka kai masa harin.
Wata majiya da ga gidan ta baiyana cewa na’urar ɗaukar hoto ce ta naɗi harin da a ka yi lokacin da shi Obiozor ɗin ba ya gidan.
Har yanzu dai Shugaban bai yi magana ba amma wani da ga cikin makusantan sa, wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce ya kira shi ya yi masa jaje.
Ya kuma yi kira ga ƴan sanda da su tashi tsaye su kamo waɗanda su ka kai harin.