Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani sabon ango tare da sace matarsa mai ciki a garin Jere da ke karamar hukumar Kagarko a jihar Kaduna.
‘Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da wasu mutane hudu na iyalan tsohon Kwamishinan Yakin Talauci na Jihar Kaduna, Abdulrahman Ibrahim Jere.
‘Yan bindigar da suka afkawa al’ummar sun haura sama da 50, inda suka mamaye al’ummar da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a kan babura.
An ce suna shiga gida gida har sai da suka gano gidan Jere wanda aka tara kila shi ne abin da suke hari.
Ko da yake tsohon Kwamishinan ya ce, baya gida lokacin da ‘yan fashin suka ziyarci gidansa, sun yi awon gaba da matarsa da wata yarinya da kanwar sa da kuma kanwar matarsa.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna (PPRO) ASP Mohammed Jalige, bai amsa kiran da ya yi masa na mayar da martani kan harin ba, ya kuma kasa amsa kiran wayarsa da aka yi masa a lokacin mika wannan rahoton. In ji The Nation.