fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan bindiga sun kashe shugaban Miyetti Allah

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders’ Association of Nigeria (MACBAN), Adamu Aliyu a unguwar Gwagwalada da ke Abuja.

An kashe Aliyu ne tare da wasu mutane hudu a kusa da kauyen Daku da ke gundumar Dobi ta karamar hukumar a ranar Alhamis.

Mohammed Usman, Sakataren MACBAN, yayin da yake tabbatar da kisan shugaban, a ranar Lahadi ya ce, an kuma yi garkuwa da mutane uku.

A cewar Usman, wasu uku sun jikkata kuma an kai su asibiti. Ya ce, marigayi shugaban MACBAN da wasu mutane shida suna dawowa ne daga Kasuwar Izom ta Jihar Neja, lokacin da aka kai masa hari.

“Suna dawowa daga Kasuwar Izom da ke Jihar Neja inda suka je sayar da shanu, sai da ya kai kilomita daya kacal zuwa kauyen Daku, kwatsam ‘yan fashin sun fito daga daji suka bude wa motar wuta, inda suka kashe shugaban MACBAN da wasu hudu,” inji shi. .

Ya bayyana sunayen wadanda aka kashen a matsayin Saleh, Aliyu, Muhammadu da Saidu, yana mai cewa an binne su kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Ya ce, jami’an tsaro suna nan a wurin kafin a yi jana’izar marigayin.

Shima shugaban karamar hukumar Gwagwalada Alhaji Adamu Mustapha ya tabbatar da faruwar lamarin.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp