fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan bindiga sun ƙona ofishin ƴan sanda suka kuma kashe mutum 2

Date:

Wasu ‘yan sanda biyu sun rasa rayukansu a safiyar ranar Asabar, yayin da wasu ‘yan bindiga suka kona shalkwatar ‘yan sandan da ke Umuguma a karamar hukumar Owerri ta yamma a jihar Imo.

Harin dai ya zo ne sa’o’i kadan bayan mataimakin babban sufeton ‘yan sanda mai kula da shiyya ta 9, a Umuahia, Isaac Akinmoyede ya bar jihar bayan wata ziyarar aiki ta kwana daya.

Hakan kuma ya faru ne kwanaki kadan bayan an kashe masu gadi biyu wadanda ke cikin rundunar hadin gwiwa ta tsaro a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai wa motar sintiri hari a Okigwe. ‘yan bindigar da isar su sun tare hanyoyin shiga da fita ta tashar, ciki har da na kusa da hedikwatar karamar hukumar.

A cewar Daily Trust, ‘yan bindigar da isar su sun tare hanyoyin shiga da fita ta tashar, ciki har da na kusa da shelkwatar karamar hukumar.

Daga nan ne suka kaddamar da harin a tashar ta hanyar jefa abun fashewa da aka inganta a cikin gine-gine, bayan sun kona ofishin, sun jira su far wa jami’an da suka gudu domin tsira da rayukansu.

Wani ganau ya ce, ‘yan sandan biyu, abin takaici, sun yi taho mu gama da ruwan harsasai. An bayyana sunayensu da kamar Ifeanyi da Iyke. An ce sun yi karatun digiri na farko a Jami’ar Jihar Imo, Owerri.

Sai dai kakakin ‘yan sandan jihar, Micheal Abattam, bai samu damar bayar da amsa ba a kan harin.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp