Kungiyar ma’aikatan lafiya ta ƙasa (MHWUN), ta ce, za ta shiga yajin aikin hadin gwiwa, domin tallafa wa kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), da sauran kungiyoyin kwadago.
Mista Biobelemoye Josiah, Shugaban MHWUN na kasa ne ya fitar da wannan barazanar a cikin wata sanarwa da ya sanya hannu tare da Mista Auwalu Kiyawa, mukaddashin babban sakataren kungiyar a ranar Lahadi a Abuja.
Bayanin yana da taken; “MHWUN na tsayawa tsayin daka da kungiyoyin da suka kafa jami’a a cikin fafutukar kwatowa da mayar da manyan makarantun gwamnati a Najeriya don samun ci gaba.”
Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa NAN, ya ruwaito cewa, ASUU da sauran kungiyoyin da ke jami’o’in gwamnati, kwalejojin fasaha da kwalejojin ilimi, sun shafe fiye da watanni shida suna gudanar da ayyukan masana’antu, bisa zargin gazawar gwamnatin tarayya wajen biyan bukatunsu.
Ƙungiyoyin suna neman tallafi na asusun farfado da aka samu alawus-alawus, da aiwatar da tsarin Haɗin Kai na Jami’ar (UTAS), da kuma bashin haɓaka.