fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi:ƴan bindiga sun kashe mutane 5 da yin garkuwa da 4 a Kaduna

Date:

Rahotanni sun ce ‘yan bindiga sun kashe biyar tare da yin garkuwa da wasu hudu a Dogon Dawa, Layin Mahuta da Tabanni da ke karamar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna.

Masu garkuwa da mutanen, a cikin mako guda, sun kuma yi awon gaba da wasu 17.

Shugaban kungiyar Birnin-Gwari Vanguard mai kula da harkokin tsaro da gudanar da mulki, Ibrahim Abubakar Nagari ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar jiya.

Ya ce: “A ranar 15 ga Maris, wasu ‘yan bindiga tare da Dogon Dawa- Zariya sun yi wa Haruna Tanko Dogon Dawa da wasu mutane biyu kisan gilla a Gabashin Birnin-Gwari.

“An yi garkuwa da wasu mutane takwas a hanya daya. A Layin Mahuta (Tabanni), wasu ‘yan bindiga sun kashe wani malamin makaranta Abdullahi Abubakar a kan hanyar Layin Lasan zuwa Tabanni a ranar 16 ga Maris.

“Yayin da a ranar 17 ga Maris, 2022, an kashe wani mutum dan shekara saba’in tare da sace mata bakwai a Layin Mahuta Tabanni. ‘Yan bindigar sun sace wasu mutane biyu a tsohuwar Tabanni.”

A yayin da ta ke yaba wa kokarin hukumomin tsaro da gwamnatin jihar Kaduna, sanarwar ta bukaci jami’an tsaro da su rinka mayar da martani a kodayaushe a kan kiraye-kirayen da ake yi a yankunan Dogon Dawa, Kuyello, Tabanni da Kutemeshi a Birnin-Gwari.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ASP Muhammad Jalige, bai amsa kiran da aka yi masa na tabbatar da faruwar harin ba ga manema labarai

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp