fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi:ƴan bindiga sun kashe mutane 5 da yin garkuwa da 4 a Kaduna

Date:

Rahotanni sun ce ‘yan bindiga sun kashe biyar tare da yin garkuwa da wasu hudu a Dogon Dawa, Layin Mahuta da Tabanni da ke karamar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna.

Masu garkuwa da mutanen, a cikin mako guda, sun kuma yi awon gaba da wasu 17.

Shugaban kungiyar Birnin-Gwari Vanguard mai kula da harkokin tsaro da gudanar da mulki, Ibrahim Abubakar Nagari ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar jiya.

Ya ce: “A ranar 15 ga Maris, wasu ‘yan bindiga tare da Dogon Dawa- Zariya sun yi wa Haruna Tanko Dogon Dawa da wasu mutane biyu kisan gilla a Gabashin Birnin-Gwari.

“An yi garkuwa da wasu mutane takwas a hanya daya. A Layin Mahuta (Tabanni), wasu ‘yan bindiga sun kashe wani malamin makaranta Abdullahi Abubakar a kan hanyar Layin Lasan zuwa Tabanni a ranar 16 ga Maris.

“Yayin da a ranar 17 ga Maris, 2022, an kashe wani mutum dan shekara saba’in tare da sace mata bakwai a Layin Mahuta Tabanni. ‘Yan bindigar sun sace wasu mutane biyu a tsohuwar Tabanni.”

A yayin da ta ke yaba wa kokarin hukumomin tsaro da gwamnatin jihar Kaduna, sanarwar ta bukaci jami’an tsaro da su rinka mayar da martani a kodayaushe a kan kiraye-kirayen da ake yi a yankunan Dogon Dawa, Kuyello, Tabanni da Kutemeshi a Birnin-Gwari.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ASP Muhammad Jalige, bai amsa kiran da aka yi masa na tabbatar da faruwar harin ba ga manema labarai

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp