fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Yara sun gano Bam a Kaduna

Date:

Mazauna yankin Shanono da ke yankin Rigasa a karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna sun sake gano wata na’urar fashewa a ranar Juma’a.

An gano na’urar sa’o’i 24, bayan an gano wani IED da aka boye a cikin bokiti a cikin al’umma.

Na’urar, wacce aka gano a ranar Alhamis, rundunar da ke yaki da bama-bamai ta jihar ce ta kwance ba tare da kuma a samu asarar rai ba.

Wani mazaunin garin, Tijjani Umar, ya ce, yara a unguwar sun gano abin da aka ajiye ranar Juma’a a cikin jarkoki da aka lullube su.

Ya ce an sanya shi kusa da rafi a cikin al’umma.

“An ajiye shi a daidai wurin da aka gano IED din ranar Alhamis. Ba mu san abin da ke faruwa a cikin wannan al’umma ba. Matar dattijona ce, ta yi gaggawar sanar da ni cewa yaran sun sake samun wani bam a cikin Jarka,” inji shi.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, ASP Mohammed Jalige, ya tabbatar da gano lamarin, inda ya ce, an hada tawagar da ke yaki da bama-bamai zuwa yankin.

“An killace yankin domin kare mutanen daga samun rauni yayin da mutanen mu ke can don kwance na’urar,” inji shi.

Ya bukaci jama’a da su kara sanya ido a duk inda suke a jihar.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp