An dage zaman taron kwamitin zartaswar jam’iyyar PDP na kasa wanda tun da farko an sanya shi a ranar 5 ga watan Mayu zuwa ranar Talata 10 ga watan Mayu.
Sen. Samuel Anyanwu, sakataren jam’iyyar na kasa ne ya bayyana hakan a daren ranar Litinin a Abuja.
Ya ce, ranar da ta gabata ta yi katsalandan ga zaben delegate na kananan hukumomi, wanda ya ce, duk ‘ya’yan jam’iyyar a bude suke, kuma ya nemi afuwar duk wani abu da ya same su.
Taron dai zai gudana ne a Sakatariyar kasa dake Wadata Plaza, Abuja, kamar yadda Anyanwu ya bayyana.
Hakazalika, kwamitin ayyuka na jam’iyyar PDP na kasa (NWC) ya jinkirta dukkan masu neman takarar gwamna da shugaban kasa daga ranar Talata, 3 ga Mayu zuwa Laraba 4 ga Mayu.
Jam’iyyar ta ce, an sauya jadawalin ne saboda bikin sallah Eid-Fitir, a cewar wata sanarwa ta biyu da sakataren yada labaranta na kasa, Mista Debo Ologunagba, ya wallafa a Abuja a daren ranar Litinin.