Wasu jami’an zabe na zanga-zangar rashin biyansu alawus-alawus na horar da su a jihar Kano.
DAILY POST ta rawsito cewa, sun hana masu kada kuri’a shiga rumfunan zabe.
Ma’aikatan wucin gadi na INEC, a yawansu, sun ce ba a biya su alawus-alawus na horar da su Naira 4000 ba.
Sun sha alwashin ba za su bari a kwashe kayan zabe ba.
Lamarin da ya afku a karamar hukumar Gwale ta jihar Kano, ya kawo tsaiko wajen fara kada kuri’a a rumfar zabe ta Dorayi Karama.