fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Gwamnonin PDP na ganawa kan rikicin Wike da Fubara

Date:

A yammacin ranar Talata ne gwamnonin jam’iyyar PDP suka hallara a Abuja domin wani taron gaggawa.

An tattaro cewa an kira taron ne kan rikicin da ke faruwa a jihar Ribas, inda wasu ‘yan majalisar dokokin jihar suka fara yunkurin tsige Sim Fubara, gwamnan da aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP.

Yanzu haka dai gwamnonin PDP na can a masaukin gwamnonin jihar Oyo da ke Abuja domin taron gaggawa.

Wasu ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas sun yi yunkurin tsige Fubara tsakanin daren Lahadi zuwa safiyar Litinin.

Wasu daga cikin gwamnonin PDP da ake ganin za su iso sun hada da Fubara, Bala Mohammed, Bauchi, Caleb Muftwang, Plateau, Dauda Lawal, Zamfara, da Ahmadu Fintiri, Adamawa.

Sauran sun hada da Ademola Adeleke na Osun, Agbu Kefas, Taraba, Godwin Obaseki, Edo da Sheriff Oborevwori, Delta.

Mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa karkashin jagorancin shugaban riko, Iliya Damagum, sun isa wurin taron.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp