Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a kananan hukumomin Jema’a da Kaura tare da fara aiki nan take biyo bayan shawarwarin da jami’an tsaro suka bayar, bayan wani hari da wasu da ake kyautata zaton Fulani ne suka kai wa yankin Agban Kagoro da kewaye wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi.
Sanarwar da Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya fitar ta bayyana cewa, “Bayan shawarwarin da hukumomin tsaro suka bayar, gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a kananan hukumomin Jema’a da Kaura tare da fara aiki nan take. Hakan na nufin taimaka wa jami’an tsaro wajen daidaita al’amura a yankunan, da ceton rayuka da dukiyoyi da kuma ba da damar maido da doka da oda.”
Sanarwar ta kuma bayyana cewa hukumomin tsaro na da cikakken ikon aiwatar da dokar hana fita.
Gwamnati ta yi kira ga daukacin mazauna kananan hukumomin Jema’a da Kaura da su ba jami’an tsaro hadin kai a aikin gaggawa na maido da zaman lafiya da bin doka da oda.
Sai dai gwamnatin, a cewar sanarwar, ta yi Allah-wadai da tashe-tashen hankula da duk wasu ayyukan rashin bin doka da ya afku a yankin.