fidelitybank

Da Ɗumi- Ɗumi: An yi garkuwa da ɗan majalisa a Anambra

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta tabbatar da yin garkuwa da Okechukwu Okoye, dan majalisa mai wakiltar mazabar Aguata 1 a majalisar dokokin jihar Anambra.

An yi garkuwa da Mista Okoye, dan asalin Isuofia, al’umma daya da Gwamna Charles Soludo na jihar Anambra, a Aguata ranar Lahadi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, Toochukwu Ikenga, ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na ƙasa, NAN lamarin a ranar Lahadi.

‘Yan sandan sun ce, an samu nasarar gano bakar Siena SUV na dan majalisar, wadda yake tukawa kafin faruwar lamarin.

Mista Ikenga, mataimakin Sufeton ‘yan sanda, ya ce ‘yan sanda sun kaddamar da farautar masu garkuwa da mutane domin kubutar da dan majalisar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan ya kuma tabbatar da kisan wani dan kungiyar ’yan banga, wanda ke kan babur a garin Oko da ke Anambra a ranar Lahadi.

Mista Ikenga ya kuma ce, marigayin yana sanye ne da kayan tsaro na musamman, amma ba dan sanda ba ne.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp