fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: An samu ɓullar cutar Ƙyandar Biri a Gombe – Gwamnati

Date:

A ranar Talata ne gwamnatin jihar Gombe, ta ayyana bullar cutar kyandar Biri a jihar, bayan wasu mutane uku da ake zargin sun kamu da cutar sun dawo lafiya.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Habu Dahiru, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai, ya ce, daga cikin mutane 19 da ake zargin sun kamu da cutar ne da aka kai ma’aikatar lafiya ta jihar, an gano samfura uku na dauke da cutar.

“Mutane guda uku da aka gabatar mana suna fama da zazzabi wanda ya dauki sama da mako guda duk da maganin da ke haifar da zazzabi. Haka kuma sun samu rabe-rabe a fuska da sauran sassan jikinsu wanda hakan ya sa ake zargin cutar kyandar biri,” inji shi.

Ya kara da cewa, “Bisa la’akari da abubuwan da suka faru a sama, na sanar da bullar cutar kyandar biri a jihar Gombe.”

KARANTA WANNAN: Cutar ƙyandar Biri na bazuwa ta hanyar jima’i – Birtaniya

Dahiru, ya ce, dukkan mutane ukun da aka tabbatar sun kamu da cutar tun daga lokacin an yi musu magani kuma an sallame su daga asibiti.

Ya ce, ma’aikatar za ta yi cikakken alhakin sa ido da amsa mai inganci da nufin shawo kan barkewar cutar.

Kwamishinan ya bayyana cewa, cutar kyandar biri, cuta ce ta zonotic da ba kasafai ake samun kamuwa da ita ba tare da daukar tsawon kwanaki 5-21, wanda ke da alamomi biyu da suka hada da zazzabi, ciwon kai, ciwon jiki da rauni.

Ya ambaci wasu alamomin da suka hada da; kumburin jiki wanda ke farawa daga fuska sannan daga baya ya bazu zuwa wani bangare na jiki, gami da tafin hannu da tafin kafa.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp