fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: An haramta cin naman Shanu a Lokoja

Date:

A ranar Alhamis din da ta gabata ne aka shawarci mazauna jihar Kogi da su guji cin naman shanu na akalla mako guda, sakamakon mutuwar shanu 20 a Lokoja.

Gwamnatin jihar ta ce, akwai yiyuwar shanun sun sha guba a lokacin da suke kiwo.

Daraktan Kula da Dabbobi na Ma’aikatar Gona ta Kogi, Dakta Salau Tarawa ne ya ba da wannan shawarar a wani taron manema labarai.

Ya ce, tuni naman shanun ya kasance a kasuwannin Lokoja, amma an dawo da shi.

Ya ce, tuni aka kai wasu shanun zuwa kasuwannin garin Osara a karamar hukumar Adavi; zuwa Ajaokuta, zuwa Obajana, zuwa Kotonkarfe da Kakanda domin sayarwa ga jama’a.

Ya kuma ce, ma’aikatar tana hada kai da jami’an tsaro domin gurfanar da makiyayan a gaban kotu.

Da yake tofa albarkacin bakinsa, shugaban sashen Agro Rangers na jihar Kogi na hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC), Bayode Emmanuel, ya ce, an gano shanun ne a Lokoja.

“Shanun sun fito ne daga bayan harabar sakatariyar jihar, inda suka je kiwo. Ba zato ba tsammani, sai suka fara nuna wani hali, suka yi kasala suka mutu cikin mintuna.

Emmanuel ya tabbatar da cewa hukumar NSCDC za ta binciki lamarin sosai,.domin sanin inda matattun shanun suka yi kiwo da kuma hana sayar da naman da suka kamu da cutar.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp